Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Hukumar Yaki Da Cin Hanci Ta Jihar Kano Ta Gayyaci Ganduje Kan ‘Bidiyon Dala’

Hukumar yaki da cin hanchi da Rashawa ta jihar Kano, ta ce
ta gayyaci tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje
domin jin bayanai a kan wani faifan bidiyon da aka taba saki,
inda ake zargin shi da karbar daloli ya na cusawa cikin aljihun
sa.

Idan dai ba a manta ba, a watan oktoba na shekara ta 2018 ne Jaridar Daily Nigerian ta wallafa wani bidiyo da ake zargin Ganduje ne a ciki ana mika ma shi kudi ya na karba.

Biyo bayan alkawarin da ya yi na bin doka da oda game da binciken da ake yi a kan bidiyoyin da ake zargin Ganduje ya na karbar daloli, shugaban hukumar Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado ya ce hukumar ta aike wa tsohon gwamnan sammaci domin ya bayyana a gaban ta.

Rimin Gado ya fara sanar da batun gayyatar Ganduje ne yayin wata tattaunawa da shi a wani shiri na gidan talabijin na Channels, inda ya ce hukumar ta na sa ran Ganduje ya bayyana a gaban ta mako mai zuwa domin samun damar gyara sunan sa a kan binciken da ake yi.

Exit mobile version