Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Gwamnan Jihar Filato Ya Bukaci A Hukunta Wadanda Ke Da Hannu A Harin Mangu

Gwamnatin jihar Filato, ta bukaci hukumomin da ke da
hurumin kamo wadanda ke da hannu a kashe-kashen da aka yi
a karamar hukumar Mangu da kewaye su bayyana wadanda su
ka kama don a hukunta su.

Gwamnan Lalong ya kuma yi alkwarin tallafa wa dubban jama’ar da ke gudun hijira sakamakon rikicin.

Matasa da mata daga sassa daban-daban na jihar Filato dai sun taru wuri guda, domin nuna alhinin su a kan kashe-kashen da kuma bayyana bukatar gwamnati ta kawo karshen hare-haren da ake kai wa mutane.

Sama da Mutane 100 ne bayanai ke nuna cewa sun hallaka a hare-hare da aka kai karamar hukumar Mangu, yayin da dabbobi da dama su ka salwanta, sannan gidaje masu tarin yawa da wuraren ibada an kona su.

Exit mobile version