Jigo a jam’iyyar APC Sanata Abu Ibrahim, ya ce babu wani dan takara daga kudancin Nijeriya da zai iya ja da Bola Ahmed Tinubu a zaben shekara ta 2023.
Sanata Ibrahim, ce wadanda ake ganin za su nemi shugabancin Nijeriya a yankin kudu maso yamma ‘yan’uwan Tinubu ne kuma ba za su yi takara da shi ba.
Ya ce Tinubu ya taka rawa wajen dawowar Kayode Fayemi a kan mulki karo na biyu, kuma shi ya dauko Osinbajo ya dora a kan kujerar mulki a shekara ta 2015.
Sanatan ya kara da cewa, lokaci ya yi da ya kamata a mara wa kudirin Tinubu baya domin ya taka gagarumar rawar a zo a gani.