Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

EFCC Ta  Ƙaddamar Da Gidan Rediyo

images 2024 02 22T201133.166

images 2024 02 22T201133.166

Gwamnatin Tarayya da Hukumar Yaƙi Da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Ƙasa Zagon Ƙasa,

EFCC, sun sha alwashin daƙile yaɗuwar labaran ƙarya a Najeriya.

Ministan Yaɗa Labarai , Mohammed Idris da shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukoyede ne suka bayar da wannan tabbacin,

yayin da suke ƙaddamar da gidan rediyon EFCC da ke kan mita 97.3 a zangon FM a Abuja a hukumance.

Muhammad Idris ya ce kamata ya yi a yaba wa hukumar kan yadda take yaƙi da cin hanci da rashawa .

Ministan ya ƙara da cewa babu wani ɗan Najeriya a yau da zai yi watsi da tasirin da EFCC ke yi.

Ya yaba da shirin gidan Rediyo da hukumar ta yi, inda yace za a ba ta cikakken ikon daƙile yaɗuwar jita-jita

Ya kuma bai wa hukumar tabbacin samun ƙarin goyon baya a ayyukan gidan rediyo da sauran ayyukan hukumar.

Exit mobile version