Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Da Sauran Kallo: Kotun Tarayya Ta Ba Gwamna Wike Iznin Karɓar Harajin VAT

Wike VAT Collation Law

Rikici ya kaure tsakanin Gwamnatin Tarayya da Gwamnatin Jihar Rivers, bayan Babbar Kotun Tarayya da ke Fatakwal ta kwace ikon karɓar harajin Jiki-Magayi na ‘VAT’ a Jihar Rivers daga hannun Hukumar Tara Haraji ta Kasa ta damƙa wa gwamnatin jihar.

Hakan ya sa nan da nan Gwamna Nysom Wike ya sanya hannu a kan dokar da Jihar za ta fara karɓar harajin VAT, kuma ta hana a riƙa ba Gwamnatin Tarayya haraji ta hannun hukumar tara haraji ta kasa.

Haka kuma, Kotun ta yanke hukuncin cewa, Gwamnatin Jihar Rivers ke da ikon karɓar duk wani haraji a fadin jihar ba Gwamnantin Tarayya ba.

Wanann hukunci kenan ya na nufin an hana Gwamnatin Tarayya karɓar kuɗaɗen haraji a jihohi. 

Exit mobile version