Home Labaru Da Sauran Kallo: Kotun Tarayya Ta Ba Gwamna Wike Iznin Karɓar Harajin...

Da Sauran Kallo: Kotun Tarayya Ta Ba Gwamna Wike Iznin Karɓar Harajin VAT

308
0
Wike VAT Collation Law

Rikici ya kaure tsakanin Gwamnatin Tarayya da Gwamnatin Jihar Rivers, bayan Babbar Kotun Tarayya da ke Fatakwal ta kwace ikon karɓar harajin Jiki-Magayi na ‘VAT’ a Jihar Rivers daga hannun Hukumar Tara Haraji ta Kasa ta damƙa wa gwamnatin jihar.

Hakan ya sa nan da nan Gwamna Nysom Wike ya sanya hannu a kan dokar da Jihar za ta fara karɓar harajin VAT, kuma ta hana a riƙa ba Gwamnatin Tarayya haraji ta hannun hukumar tara haraji ta kasa.

Haka kuma, Kotun ta yanke hukuncin cewa, Gwamnatin Jihar Rivers ke da ikon karɓar duk wani haraji a fadin jihar ba Gwamnantin Tarayya ba.

Wanann hukunci kenan ya na nufin an hana Gwamnatin Tarayya karɓar kuɗaɗen haraji a jihohi. 

Leave a Reply