Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

COVID-19 Ta Kashe 28, Ta Kama 873 A Najeriya

Annobar COVID-19 ta kashe mutum 28 a Najeriy zuwa yanzu

Annobar COVID-19 ta kashe mutum 28 a Najeriy zuwa yanzu

Annobar coronavirus ta kama mutum 873 a Najeriya bayan karin mutum 91 sun kamu da cutar a rana guda.

Cutar ta kashe mutum 28 a Najeriya inda wasu 648 ke kwance a asibiti, baya ga wasu mutum 197 da suka warke, ya zuwa karfe 11:25 na daren Laraba, 22 ga Afrilu, 2020.

Mutum 74 ne suka kamu da cutar a ranar Laraba a jihar Legas, inda cutar ta fi kamari.

Akwai kuma karin mutum 5 a Katsina, da wasu 4 a Ogun, a cewar Cibiyar Hana Yaduwar Cututtuka ta Najeriya NCDC.

Cibiyar ta ce a jihar Delta an samu karin mutum 2, da kuma 2 a Edo. Akwai kuma mutum daya-daya a jihohin Kwara, Oyo, Adamawa da kuma Abuja.

Alkaluman COVID-19 da NCDC ta fitar sun nuna cewa a jihar Legas ce aka fi samun wadanda suka kamu da cutar a Najeriya da wayan mutum fiye da 504 da kuma sauran jihohin kamar haka:

  1. Lagos – 504
  2. Abuja -119
  3. Kano – 73
  4. Ogun – 24
  5. Katsina – 21
  6. Osun – 20
  7. Oyo – 17
  8. Edo – 17
  9. Kwara – 10
  10. Kaduna – 9
  11. Akwa-Ibom – 9
  12. Borno – 9
  13. Bauchi – 8
  14. Delta – 6
  15. Gombe – 5
  16. Ekiti – 4
  17. Ondo – 3
  18. Rivers – 3
  19. Jigawa – 2
  20. Enugu – 2
  21. Niger – 2
  22. Abia – 2
  23. Benue – 1
  24. Anambra – 1
  25. Sokoto – 1
  26. Adamawa-1

Hakan na zuwa ne washegarin ranar da mutum 117 suka maku da cutar a rana guda a kasar.

Exit mobile version