Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Buhari Ya Taya Tinubu Murnar Shugabancin ECOWAS

Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya taya shugaba
Bola Tinubu murnar zaɓen sa da aka yi a matsayin shugaban
kungiyar bunƙasa arzikn Afirka ta Yamma ECOWAS.

Kakakin tsohon shugaban kasa Malam Garba Shehu ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.

Garba Shehu, ya ce al’ummar Afirka ta Yamma sun damƙa wa sabon shugaban Nijeriya gagarumin aiki, don haka akwai bukatar a taimaka ma shi don ganin bai bada kunya ba.

Buhari ya kara da cewa, ya na fatan Allah ya sa a farfaɗo da ECOWAS a matsayin ƙungiyar tabbatar da dimokraɗiyya, da kyakkyawan shugabanci da yaki da ta’addanci da sauyin yanayi a zamanin mulkin Tinubu.

Exit mobile version