Kungiyar tabbatar da adalci da kuma shugabanci na gari wato SERAP, ta ce ta na goyon hukumar EFCC a kan binciken da za ta yi wa tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, kan kudin Lantarki naira billiyan 16.
Kungiyar ta ce wannan wata dama ce da hukumar yaki da rashawa za ta yi amfani da shi na kawar da zargin cewar ba a binciken masu manyan matsayi a Najeriya.
A cikin wata sanarwa da mataimakin daraktan kungiyar Kolawale Oluwadare, ya fitar, ta ce binciken ya zo kan gaba musamman a lokacin da al’ummar Najeriya suka matsu wajen ganin ana binciken zarge-zargen cin hanci da rashawa da kuma take hakkin dan adam.
Kungiyar ta ce binciken wani abu ne da ta dade ta son ganin ana gudanar wa, musamman akan yadda ‘yan Najeriya suka zaku suke son ganin an gudanar da bincike a bangaren, saboda matsalar da suke fuskanta na rashin wutar lantarki, duk da cewar suna biyan kudin wuta.