Gwamnatin jihar Kaduna ta sa dokar hana fita ta Sa’o’i 24 a
unguwannin Sabon Garin Nassarawa da Tirkaniya da ke
yankin ƙaramar hukumar Chikun.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan tsaro da al’amuran
cikin gida na jihar Kaduna Samuel Aruwan ya fitar, ya ce an
ɗauki matakin ne bayan wani rikicin ‘yan sara-suka ya yi
sanadiyyar mutuwar mutane biyu.
Sanarwar, ta umarci jami’an tsaro su tabbatar da dokar a
unguwar, domin maido da zaman lafiya yayin da ake ci-gaba
da bincike don gano musabbabin abin da ya haddasa hargitsin.
Kwamishinan tsaron ya yi kira ga mazauna yankin su yi
biyayya ga dokar, wadda ta fara aiki nan take.

