Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

An Kashe Mutane 201 A Filato Cikin Watanni 5

Akalla mutane 201 ne aka bada rahoton sun mutu cikin watanni biyar a hare-hare 27 da aka kai kananan hukumomi 7 na jihar Filato kamar yadda rahotanni su ka ruwaito.

Jihar Filato dai ta na fama da hare-hare na ‘yan ta’adda da rikice-rikicen kabilanci, inda kwanan nan aka sa dokar hana fita ta sa’o’i 24 a karamar hukumar Mangu sakamakon rikicin kabilanci.

Kashe-kashen dai sun auku ne daga ranar 19 ga watan Janairu zuwa ranar 20 ga watan Yuni na shekara ta 2023.

Kanana hukumomin da lamarin  ya shafa kuwa sun hada da Riyom da Bokkos da Jos  ta Kudu da Jos ta Gabas da Barkin Ladi da Bassa da kuma Mangu.

Exit mobile version