Home Labaru Zaben Kogi: INEC Ta Ce Za Ta Dauki Ma’aikatan Wucin-Gadi Dubu 16...

Zaben Kogi: INEC Ta Ce Za Ta Dauki Ma’aikatan Wucin-Gadi Dubu 16 Da 139

287
0
Hukumar Zabe Mai Zaman Kan Ta kasa, INEC
Hukumar Zabe Mai Zaman Kan Ta kasa, INEC

Hukumar zabe mai zaman kan ta ta kasa INEC, ta ce za ta dauki ma’aikatan wucin-gadi dubu 16 da 139, domin gudanar aikin zaben gwamnan jihar Kogi da za a yi ranar 16 ga watan Nuwamba.

Kakakin hukumar zabe ta kasa Festus Okoye ya bayyana haka,  yayin wani shirin sanin makamar aiki da horarwa da aka gudanar a kwalejin gwamnatin tarayya da ke Okene.

Ya ce hukumar zabe na bukatar wannan adadi na ma’aikata, domin zaben gwamnan jihar Kogi da za a gudanar a rumfunan zabe dubu 2 da 548 a cikin unguwanni 239 na jihar.

Festus Okoye ya kara da cewa, yayin da ake daf da kammala duk wani shiri, nan da mako biyu duk kayayyakin zaben za su kasance a jihar.

Leave a Reply