Home Home Zaben 2023: Gwamna Wike Na Rivers Zai Nemi Shugabancin Najeriya

Zaben 2023: Gwamna Wike Na Rivers Zai Nemi Shugabancin Najeriya

238
0
Gwamna Nyesom Wike na Jihar Rivers ya ayyana muradin sa na neman shugabancin Najeriya, yana mai cewa yana da ƙwarewar da zai lashe zaɓen 2023 a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar adawa ta PDP.

Gwamna Nyesom Wike na Jihar Rivers ya ayyana muradin sa na neman shugabancin Najeriya, yana mai cewa yana da ƙwarewar da zai lashe zaɓen 2023 a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar adawa ta PDP.

Gwamna Wike, ya bayyana haka ne yayin ganawar da ya yi da shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Benue a gidan gwamnatin jihar da ke Mukudi a ranar Lahadi.

Wike, ya nemi wakilan jam’iyyar su jefa masa ƙuri’a a zaɓen fitar da gwani yana mai jaddada batun karɓa-karɓa.

Ya ce matukar ana bukatar korar jam’iyyar APC daga kan karagar mulki, to shi kadai ne zai iya.

Ya ƙara da cewa dole ne su ƙwace mulki, kuma ya shirya yin hakan a jam’iyyar PDP domin Allah yana tare da su, shi ya sa APC ke taɓarɓarewa a koyaushe.

Leave a Reply