Home Labaru Yanke Hukunci: Bulkachuwa Ta Gargadi Lauyoyi Su Daina Azarbabi

Yanke Hukunci: Bulkachuwa Ta Gargadi Lauyoyi Su Daina Azarbabi

332
0
Zainab Bulkachuwa, Shugabar Kotun Daukaka Kararrakin Zaben Shugaban Kasa

Shugabar kotun daukaka kararrakin zaben shugaban kasa, Zainab Bulkachuwa ta yi barazanar cewa za ta yi maganin lauyoyi masu kai korafe-korafe ga ’yan jarida da kuma yin sharhi akan karar da ke a gaban kotun.

Bulkachuwa, ta ce duk lauyan da aka kama ya na sharhin kararrakin a kafafen yada labarai bayan zaman kotu, to kotun daukaka kara za ta yi maganin sa.

Zainab mai shari’a ta bayyana hakan ne a lokacin da take gargadin a wurin kaddamar da fara zaman kotun a Abuja, ta ce irin wadannan rubuce-rubucen da sharhin na kawo wa kotu cikas da kuma tarnaki ga yanke hukunci tare  da jefa waswasi ga jama’a a kan hukuncin da kotu za ta yanke.

Bulkachuwa, ta kara da cewar wasu na rubuce-rubuce a shafin yanar gizo ko surutai a gidajen radiyo da talbijin su na yanke hukuncin mai laifi da mai gaskiya a  wasu shari’o’in da ke gaban kotu da ba a rigaya aka yanke musu hukunci ba. Daga karshe shugabar kotun daukaka kararrakin zaben ta ce wannan gargadi bai tsallake kan jam’iyyun siyasa da magoya bayan su ba.