Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Yajin Aiki: Ayyukan Bangaren Kiwon Lafiya A Najeriya  Sun Shiga Halin Ha’ula’i

Shugaban kungiyar likitocin Najeriya Dr. Orji Emeka Innocent, ya ce yajin aikin da kungiyar likitocin Najeriya NARD ta fara ya jefa harkoki da cibiyoyin kiwon lafiyar jama’a a Najeriya cikin halin ha’ula’i.

Dr. Orji Emeka Innocent, ya ce ‘ya’yan kungiyar sun bi duk hanyoyin da suka dace a ƙoƙarin su na ganin an warware rikicin amma hakar su bata cimma ruwa ba.

Ya ce a asibitin koyarwa na Aminu Kano da ke Kano, an umarci mutane su mayar da ‘yan uwan su marasa lafiya gida saboda babu likita da zai duba su, yayinda a Legas kuma likitoci na ci gaba da kula da majinyatan da aka kwantar da su amma ba su karban sabbin marasa lafiya.

A halin da ake ciki dai likitoci masu neman ƙwarewa wadanda ke da kaso mafi tsoka a manyan asibitocin gwamnati, sun ce sun shiga yajin aiki ne har sai gwamnati ta biya musu bukatun su na albashi da kudin walwala.

Exit mobile version