Home Labaru Yadda Jami’An Kwastam Suka Bindige Ɗan Uwansu Jami’i A Shingen Bincike

Yadda Jami’An Kwastam Suka Bindige Ɗan Uwansu Jami’i A Shingen Bincike

240
0

Jami’an hukumar kwastam da ke aiki a wani shingen bincike a
karamar hukumar Garki ta jihar Jigawa,’a sun harbe wani
abokin aikin su da ke dawowa daga jamhuriyar Nijar bayan ya
ki tsayawa yi masa bincike.

Jami’an kwastam da ke aiki a shingen binciken dai sun shiga shakku lokacin da motar jami’in mai suna Muhammad Sayyadi ya nufo shingen, sannan ya ki tsayawa a bincike shi.

A cikin rashin sani, ashe jami’in ya na dawowa ne daga garin Magarya bayan ta’aziyyar da ya kai wa tsohon jakadan Nijeriya a Korea Ta Kudu Ali Magashi bisa rasuwar mahaifiyar sa.

Sai dai lamarin ya nemi tada hankalin mutanen yankin Ringimna, lokacin da su ka fahimci cewa Sayyadi dan Sarkin Ringim ne.

Leave a Reply