Shugabar hukumar zabe ta jihar Kaduna SIECOM Dr. Saratu Dikko Audu, ta bayyana dage zaben kananan hukumomin jihar zuwa ranar 4 ga watan Satumba na shekara ta 2021.
Dr. Saratu Dikko Audu, ta bayyana haka ne a helkwatar hukumar, yayin wani taro da su ka gudanar a Kaduna.
Tun farko dai an shirya gudanar da zaben shugabannin kananan hukumomi da kansilolin ne a ranar 5 ga watan Yuni na shekara ta 2021, kafin daga bisani a dage zuwa ranar 14 ga watan Augusta na shekara ta 2021.