Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Wa’adi Na Biyu: Matan APC Sun Bukaci Shugaba Buhari Ya Dama Da Su

Wasu matan jam’iyyar APC sun taya shugaba Muhammadu Buhari murnar gudanar da bikin ranar dimokradiyya ta Nijeriya ranar bikin farar hula a Najeriya inda a ka yi bikin murnar zarcewarsa a kan mulki.

Haka kuma, matan sun yi wa shugaba Buhari addu’o’in samun karin lafiya domin ya jagoranci Nijeriya ba tare da samun matsaloli ba a karkashin jagorancin Adedoyin Eshanumi.

Misis Eshanumi, ta jagoranci sauran takwarorin ta mata da su ka yi takara a karkashin jam’iyyar APC a zaben shekara ta 2019, domin yi wa shugaba Buhari addu’ar samun iko da basira da lafiyar mulkin Nijeriya.

Matan, sun kuma nemi shugaba Muhammadu Buhari ya rika damawa da su a sha’anin mulki cikin shekaru hudu masu zuwa, domin sun nuna wa jam’iyyar APC goyon baya a shekara ta 2019.

Eshanumi, ta ce a cikin mata 360 da su ka nemi takara a zaben da ya gabata, kasa da kashi daya ne kadai su ka yi nasara, don haka ta nemi shugaba Buharir ya tafi da su a wa’adin mulkin san a biyu.

Exit mobile version