Home Labaru Wa’adi Na Biyu: Matan APC Sun Bukaci Shugaba Buhari Ya Dama Da...

Wa’adi Na Biyu: Matan APC Sun Bukaci Shugaba Buhari Ya Dama Da Su

397
0

Wasu matan jam’iyyar APC sun taya shugaba Muhammadu Buhari murnar gudanar da bikin ranar dimokradiyya ta Nijeriya ranar bikin farar hula a Najeriya inda a ka yi bikin murnar zarcewarsa a kan mulki.

Haka kuma, matan sun yi wa shugaba Buhari addu’o’in samun karin lafiya domin ya jagoranci Nijeriya ba tare da samun matsaloli ba a karkashin jagorancin Adedoyin Eshanumi.

Misis Eshanumi, ta jagoranci sauran takwarorin ta mata da su ka yi takara a karkashin jam’iyyar APC a zaben shekara ta 2019, domin yi wa shugaba Buhari addu’ar samun iko da basira da lafiyar mulkin Nijeriya.

Matan, sun kuma nemi shugaba Muhammadu Buhari ya rika damawa da su a sha’anin mulki cikin shekaru hudu masu zuwa, domin sun nuna wa jam’iyyar APC goyon baya a shekara ta 2019.

Eshanumi, ta ce a cikin mata 360 da su ka nemi takara a zaben da ya gabata, kasa da kashi daya ne kadai su ka yi nasara, don haka ta nemi shugaba Buharir ya tafi da su a wa’adin mulkin san a biyu.