Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Tsaro: ‘Yan Sanda Sun Kama ’Yan Tada-Zaune-Tsaye 90 A Kano

Rundunar ‘yan Sanda ta Jihar Kano, ta sanar da kama wadanda ake zargi da aikata laifuffuka daban-daban har mutane 90 a makon da ya gabata.

Sabon Kwamishinan ‘yan Sanda na Jihar Ahmed Iliyasu ya bayyana wa manema labarai haka a Hedikwatar Rundunar da ke Bompai birnin Kano.

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a farmakin da jami’an tsaro su ka kai wurare da dama da aka yi zargin maboyar batagari ce.

Daga cikin wurare da garuruwan da aka kai farmakin kuwa akwai Gano a Karamar Hukumar Dawakin Kudu, Bachirawa a Karamar Hukumar Ungogo da kuma kan Titin Gidan Sarkin Kano a cikin Karamar Hukumar Birni da Kewaye.

An kuma kama wasu a Dala, da Panshekara, da Kwana Hudu da kuma Dakata duk a cikin Kano.

Daga cikin kayan lahanta jama’a da aka samu a jikin masu laifin akwai wukake 64, da almakasai da dama, da gatari, da awartakin datse karfe, da layu da guraye, da kullin tabar wiwi da kuma madarar sukudaye.

Exit mobile version