Home Labaru Takaddama: Gudunmuwar Da Buhari Yaba Kasar Guinea Ta Haifar Da Cece-Kuce

Takaddama: Gudunmuwar Da Buhari Yaba Kasar Guinea Ta Haifar Da Cece-Kuce

213
0
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari

Biyo bayan gudunmuwar dala 500,000, kwatankwacin kusan naira miliyan 180 da Shugaba Muhammadu Buhari ya ba kasar Guinea Bissau, lamarin ya haifar da cece-kuce musamman a shafukan sada zumunta na zamani.

Shugaba Muhammadu Buhari dai ya ce wannan gudummawa ce da kasar Guinea Bissau za ta yi amfani da ita domin gudanar da zabe a kasar.

Sauran kayayyakin da Nijeriyar za ta tallafa wa kasar da su kuma sun hada da akwatunan jefa kuri’a 350, da baburan hawa guda 10, da kuma motocin a-kori-kura guda biyu.

Shugaba Buhari ya umarci ministan harkokin kasashen wajen Nijeriya Geoffrey Onyeama ya wakilce shi a kasar ta Guinea.