Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Takaddama: Dankwambo Ya Yi Wa Kan Shi Gwanjon Motocin Gwamnati

Babban mai ba gwamnan jihar Gombe shawara ta fuskar watsa labarai Ismail Misilli, ya musanta zargin cewa su na yi wa tsohon gwamnan jihar bi-ta-da-kulli a kan saida kayan gwamnati na miliyoyin Naira.

A cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, Isma’il ya ce ya zama dole a shaida wa duniya cewa gwamna Inuwa Yahaya mutane ne su ka zabe shi a kananan hukumomi 11 da ke fadin jihar.

Ya ce gwamnatin jihar ta rasa gane dalilin da ya sa ake tunanin ana yi wa tsohon gwamnan jihar bi-ta-da-kulli, duk da cewa binciken ‘yan kwamitin kwato kadarorin jihar ya tabbatar da cewa, akwai hannun tsohon gwamnan a cikin saida kadarorin jihar

Isma’il ya kara da cewa, kwamitin kwato kadarorin jihar a karkashin jagorancin Peter Bilal, an dora ma shi alhakin gano yadda aka yi gwanjon kadarorin jihar a lokacin mulkin tsohon gwamnan jihar Ibrahim Dankwambo, wanda hakan ya sa dole akwai muhimman tambayoyi da za a yi.

Exit mobile version