Home Labaru Ta’addanci: Za A Yi Karancin Abinci A Jihohin Da Ake Satar Mutane...

Ta’addanci: Za A Yi Karancin Abinci A Jihohin Da Ake Satar Mutane – Masari

252
0
Masari

Gwamman jihar Katsina Aminu Bello Masari, ya ce babu makawa za a samu karancin abinci a yankuna da ke fama da ta’addancin ‘yan bindiga.

Wurare da dama dai na ci-gaba da fargabar yadda rashin tsaro ke barazana ga noma a yankunan da ke fama da garkuwa da mutane a Nijeriya,

Gwamna Masari ya bayyan haka ne, yayin wata hira da ya yi da manema labarai.

Masari ya tabo batuwa da dama da su ka shafi tsaro a yankunan jihar sa da ma na makwabta, ciki har da batun irin kokarin da gwamnatocin yankunan ke yi na kawo karshen hare-hare da ma satar mutane da ake yi.