Home Labarai Sojoji Sun Kama Kwamandan ISWAP A Neja Sun Kashe ‘Ƴan Bindiga A Kaduna

Sojoji Sun Kama Kwamandan ISWAP A Neja Sun Kashe ‘Ƴan Bindiga A Kaduna

155
0

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da kashe ƴan bindiga bakwai a Jihar Kaduna tare da ƙwato makamai.


Haka kuma wasu rahotannin na cewa sojojin sun daƙile wani hari da aka kai musu a wani sansanin su da ke Ƙaramar Hukumar Borgu ta Jihar Neja inda suka kama kwamandan ƙungiyar ISWAP.


A wani saƙo da rundunar sojin Najeriya ta wallafa a shafinta na Facebbok, ta bayyana cewa tun da farko dakarun Operation Safe Forest Sanity ne suka ƙaddamar da wani samame a Maidaro da Tudun Kagi da Kusharki da kuma Anguwan Madaki duka jihar.


A yayin samamen, sojojin sun yi musayar wuta da ƴan bindigar inda suka kashe ƴan bindigar huɗu tare da ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da harsasai samfarin 7.62mm da kuma bindiga ƙirar Pump Action ɗaya da harsasai uku da ƙananan bindigogi da babura huɗu.


A wani samame a yankunan Sabon Birni-Zartake da Ungwan Lima Riyawa da Tungan Madaki sojojin sama sun yiwa ƴan bindigar da ke tserewa daga Tudun Kagi kofara rago, tareda kashe uku daga cikin su.

Leave a Reply