Kotun sauraren kararrakin zabe da ke zama a birnin Akure na jihar Ondo, ta soke zaben Ikebgboju Gboluga, a matsayin dan majalisar wakilai daga mazabar Okitipupa da Irele a karkashin jam’iyyar PDP.
An dai soke zaben Gboluga ne, bisa dalilin cewa ba ya da hurumin yin takara a zaben ranar 23 ga watan Fabrairu na shekara ta 2019, saboda mallakar takardun zama dan asalin kasar Ingila tare da yin rantsuwar zama mai biyayya ga kasar kafin a ba shi takardun shaidar zama dan kasa.
Kotun,
ta bayyana sunan Albert Akintoye na jam’iyyar APC a matsayin halastaccen wanda
ya lashe zaben, tare da ba hukumar zabe ta kasa umarnin ta karbe shaidar cin
zabe daga hannun Gboluga ta ba Akintoye.