Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Shari’a: Kotu Ta Umarci DSS Ta Biya Sowere Diyyar Kamen Sa Kan Zanga-Zangar Revolutionnow

Babbar kotun tarayya Abuja, ta ayyana kamun da aka yi wa mawallafin jaridar Sahara kuma jagoran zanga-zangar juyin-juya hali Omoyele Sowere a matsayin haramtacce, tare da bukatar biyan sa diyyar cin zarafin da aka yi ma shi.

Babbar kotun tarayya Abuja, ta ayyana kamun da aka yi wa mawallafin jaridar Sahara kuma jagoran zanga-zangar juyin-juya hali Omoyele Sowere a matsayin haramtacce, tare da bukatar biyan sa diyyar cin zarafin da aka yi ma shi.

Umarnin alkalin kotun dai ya na zuwa ne, makonni uku bayan wata babbar kotu a karkashin jagorancin mai shari’a Chikere Anwuli ta Umarci hukumar tsaro ta DSS ta biya Sowore naira miliyan biyu sakamakon karbe ma shi wayar hannun sa yayin da aka kama shi.

A hukuncin kotun, alkalin ya kuma bada umarnin a saki wasu mutane biyu da ake zargin su na da hannu wajen mara wa Sowore baya a zanga-zangar da ya yi wa lakabi da #RevolutionNow a Turance.

Tuni dai lauyoyin Sowore da su ka hada da Marshar Abubakar da Femi Falana, sun ayyana hukuncin a matsayin bayyanar gaskiya kuma abin kunya ga hukumar tsaro ta DSS.

Exit mobile version