Home Labaru Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken Ya Tattauna Da Tinubu

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken Ya Tattauna Da Tinubu

100
0

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken, ya
tattauna da zababben Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ta
wayar tarho.

Wata sanarwa da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Matthew Miller ya fitar a shafin yanar gizo, ta ce tattaunawar da su ka yi ta karkata ne a kan yadda Amurka da Nijeriya za su kara yaukaka dangantakar su.

Ta ce Sakataren harkokin wajen Amurka ya tattauna da Tinubu ne don ya kara nuna shirin Amurka na ci-gaba da karfafa dangantakar ta da gwamnatin Nijeriya mai jiran gado.

Sanarwar ta kara da cewa, an gina kawancen kasashen biyu ne a kan wasu muradu da su ke girmamawa, da kuma kyakkyawar alakar da ke tsakanin al’ummar kasashen biyu, sannan akwai bukatar alakar ta dore a karkashin Bola Ahmed Tinubu.

Blinken da Tinubu, sun kuma tattauna a kan muhimmancin shugabancin da zai dama da daukacin ‘yan Nijeriya, da hadin kai a fannin tsaro da samar da sauye-sauye domin tallafa wa fannin tattalin arziki.

Leave a Reply