Shugaban kungiyar yankin Niger Delta Asari Dokubo, ya karyata gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, a game da maganar ruguza wani masallaci a jihar.
Karanta Wannan: Kanjamau: Za A Rika Karbar Magani Kyauta A Jihar Rivers – Wike
Dokubo, ya bayyana cewa babu shakka Nyesom Wike ya rusa wannan babban masallaci na Trans-Amadi da ake magana da ke cikin a Fatakwal.
Ya ce gwamnatin jihar Rivers ta na ikirarin cewa ba ta ruguza wani masallaci ba, amma a wani bidiyo da ke yawo a kafafen zamani, an nuna yadda katafila ke rushe masallacin.
Asari Dokubo, ya kara da cewar Nyesom Wike, ya na ikirarin cewa babu masallaci, saboda haka karya ce, yake yi domin idan babu masallaci me ya kai ka wurin.
Ya ce wanda ya saye filin masallacin mutumin Okrika ne ‘Dan kabilar Ijaw mai suna Dr. Sotonye Amadi.