Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Rikicin Zamfara: Kungiyar Masu Hakar Ma’adinai Ta Ce Za Su Ba Gwamnati Hadin Kai

Kungiyar masu hakar ma’adinai ta Nijeriya, ta ce za ta ba gwamnatin tarayya hadin kai, dangane da umurnin da ta bada na tsaida ayyukan hake-haken ma’adanai a jihar Zamfara.

Shugaban kungiyar na kasa Alhaji Kabir Kankara ya bayyana haka a Abuja.

Gwamnatin Tarayya dai ta bada umurnin dakatar da ayyukan hake-haken ma’adanai a jihar Zamfara ne ranar 7 ga watan Afrilu.

Shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya Muhammed Adamu, ya ce umurnin ya na daga cikin matakan da aka dauka na magance lamarin ta’addanci a jihar Zamfara.

Alhaji Kabir Kankara, ya ba gwamnati da hukumomin ta tabbacin cewa, a shirye kungiyar ta ke ta ba su hadin kai domin tabbatar da zaman lafiya da kwazo a fannin hakar ma’adanai.

Exit mobile version