Home Labaru Rikicin Sudan: Alkalumman Wadanda Su Ka Mutu Na Cigaba Da Karuwa

Rikicin Sudan: Alkalumman Wadanda Su Ka Mutu Na Cigaba Da Karuwa

380
0

Jami’an tsaron kasar Sudan na kokarin tabbatar da ikon su a babban birnin Khartoum bayan hallaka sama da farar hula 100, wadanda ba su dauke da wani makami yayin tarwatsa masu zanga-zangar tabbatar da dimokradiyya.

Kungiyoyi masu adawa na cewa an samu karin mutanen da aka jefa a cikin wani kogi.

An tsinkayi dakarun wata kungiyar mayakan sa-kai ta gwamnati da ake jin tsoron su, su na ta sintiri a birnin, inda rahotanni ke cewa su na harbi da bugu da kuma kama fararen hula.

Haka kuma, ana ganin a ‘yan kawanaki kadan da su ka gabata, ‘yan hamayyar na Sudan ke dab da cimma yarjejeniya da sojojin da ke rikon-kwarya na kasar a kan kafa gwamnatin farar-hula, amma kwatsam al’amurra su ka tabarbare.

Dakaru masu alaka da gwamnati da ke tarwatsa masu zanga-zangar da su ka yi zaman dirshan dai, sun yi nasarar korar wasu fararen hula, lamarin da ya kai ga sun bar dandalin da su ka mamaye zuwa cikin unguwanni.