Home Labaru Rikicin Shi’a: Kotu Ta Dage Sauraren Shari’ar El-Zakzaky Ta Neman Beli

Rikicin Shi’a: Kotu Ta Dage Sauraren Shari’ar El-Zakzaky Ta Neman Beli

478
0
Ibraheem El-Zakzaky, Shugaban Kungiyar Shi’a Ta Nijeriya
Ibraheem El-Zakzaky, Shugaban Kungiyar Shi’a Ta Nijeriya

Babbar kotun Kaduna da ke sauraren bukatar neman belin shugaban kungiyar shi’a Malam Ibrahim Elzakzaky da mai dakin sa, ta dage sauraren karar zuwa ranar 5 ga watan Agusta domin yanke hukunci.

Yayin zaman kotun, lauyan El-Zakzaky Femi Falana ya shaida wa kotun cewa, mutumin da ya ke karewa ya na cikin matsanancin halin rashin lafiyar, wanda ke bukatar a fitar da shi kasar waje domin nema masa magani.

Lauyan El-Zakzaky Femi Falana

Ya ce a kasar waje ne kawai za a iya duba Sheikh Ibrahim El-Zakzaky yadda ya kamata saboda tsanantar da cutar ta yi.

Sai dai lauyan gwamnati Debris Bayero ya soki uzurin da Femi Falana ya gabatar a gaban kotun, inda ya ce ba sai an fitar da El-Zakzakky kasar waje ba, kasnacewar akwai kwararrun likitocin da za su iya duba shi a cikin gida.