Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sabonta alkawarin cewa gwamnatin tarayya za ta magance lamarin rashin tsaro a Najeriya.
Dan majalisar dattawa mai wakiltan yankin Sokoto ta arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayyana hakan ne a madadin shugaban kasa a lokacin da ya kai ziyara ga wadanda harin yan bindiga ya rutsa da su a karamar hukumar Goronyo dake jihar Sokoto.
Wamakko ya mika kayayyakin tallafi ga shugaban jam’iyyar All APC a karamar hukumar Goronyo, Kabitu Sarki Fulanin Goronyo, domin a rarrabawa mutanen da abin ya shafa.
Hare-haren ya janyo mutuwar mutane 29, a yayin da wasu kuma suka bar gidanjensu a yankin.