Home Labarai Ohaneze Ta Umarci Al’Ummar IGBO Su Kaurace Wa Zanga-Zanga

Ohaneze Ta Umarci Al’Ummar IGBO Su Kaurace Wa Zanga-Zanga

81
0
16216173 1664795409544 jpeg85cff5f120c5880c81533e97d9ec7802
16216173 1664795409544 jpeg85cff5f120c5880c81533e97d9ec7802

Ohaneze, ta umarci ’yan kabilar a fadin Najeriya su kaurace wa zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa da ake shirin yi.

Wata sanarwa da Mazi Okechukwu Isiguzoro ya fitar a ranar Talata ta ce kungiyar Ohaneze Ndigbo ta gargadi masu zanga-zangar.

Ya bayyana cewa a tsawon tarihi, ’yan kabilar Igbo ’yan kabilar Igbo ne suka fi shan wahala bayan duk wata gagarumar zanga-zanga

a fadin Najeriya inda suke asarar rayuka da dukiyoyin su a fadin kasa.

Sanarwar ta ce, na farko dai, kalubalen tsaro da ake fama da shi a yankin Kudu maso Gabas zai hana gudanar da zanga-zanga a cikin aminci.

Isiguzoro ya kara da cewa zanga-zangar za ta kara ta’azzara matsalolin tsaro da ake fama da su a yankin Kudu maso Gabas,

Sannan za ta ba da dama ga masu aikata laifuka da makiyan al’ummar Igbo su yi amfani da zanga-zangar wajen haifar da rudani.

Leave a Reply