Home Labaru Nasara: Jami’an Tsaro Sun Fara Samun Bayanan Sirri Daga ‘Yan Kasa A...

Nasara: Jami’an Tsaro Sun Fara Samun Bayanan Sirri Daga ‘Yan Kasa A Nijar

139
0
Rundunar hadin gwiwar G5 Sahel ta sanar da samun nasarar kama wasu ‘yan ta’adda sama da 10 a yankin iyakokin kasashen Nijer, Burkina, Faso da Mali bayan da ta bi diddigin wasu bayanan da ta samu daga al’ummar kauyukan jihar Tilabery.

Rundunar hadin gwiwar G5 Sahel ta sanar da samun nasarar kama wasu ‘yan ta’adda sama da 10 a yankin iyakokin kasashen Nijer, Burkina, Faso da Mali bayan da ta bi diddigin wasu bayanan da ta samu daga al’ummar kauyukan jihar Tilabery.

Masu fafutuka suna ganin wannan al’amari a matsayin wani babban ci gaba a yaki da ta’addanci amma kuma suka ce wajibi ne hukumomi su dauki matakin kare duk wanda ya ke tsegunta bayanai na sirri.

A sanarwar da ta fitar rundunar hadin gwiwar G5 Sahel ta ce sakamakon wasu bayanan da wata bataliyar sojojin Nijer da ke da sansani a kauyen Wanzarbe na gundumar Tera ta samu daga mazauna kauyen Balley Koira sun bada damar cafke wasu ‘yan ta’adda 9 dauke da shanu 18 da babur 1 sabo ful da suke shirin batarwa a kasuwar kauyen na Balley Koira dake a tazarar km 30 a kudu maso gabashin Wanzarbe.

Wannan wata alama ce dake nunin an fara samin canjin tunani a wajen al’umar yankin da wani lokaci ake zargi da hada kai da ‘yan ta’adda inji wani mai bin diddigin al’amuran yau da kullum Ibrahim Kantama.

Leave a Reply