Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Mu Hada Kai Don Tinubu Ya Zama Shugaban Kasa – Sanwo-Olu

Gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, ya yi kira ga shugabannin jam’iyyar APC su hada kai da juna domin ganin Bola Tinibu ya samu nasarar zama shugaban kasa.

Sanwo-Olu ya bayyana haka ne, yayin da ya kai ziyarar aiki kananan hukumomin Amuwo-Odofin da Oriade a ranar Larabar da ta gabata.

Ya ce akwai bukatar su sadaukar da kan su domin ganin mulki ya hannun hannun Yarbawa.

Gwamnan, ya kuma yi kira ga dukkan Sarakuanan gargajiya su hada kai da gwamnonin kananan hukumomi a dukkan al’ummar Inyamurai kudu da Arewa.

Exit mobile version