Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Matsalar Tsaro: Masari Ya Bukaci Tallafin Gwamnatin Tarayya

Aminu Bello Masari, Gwamnan Jihar Katsina

Aminu Bello Masari, Gwamnan Jihar Katsina

Gwamna Aminu Bello Masari na jihar Katsina, ya bukaci gwamnatin tarayya ta samar da kudaden da za a tallafa wa mutanen da rikicin ‘yan bindiga ya rutsa da su a jihohin Sokoto da Zamfara da kuma Katsina.

Masari ya yi rokon ne, a wajen taron jin ra’ayoyin al’umma na kwana daya da Ma’aikatar Sadarwa ta Tarayya ta yi dangane da tsaro a Katsina.

Gwamna Masari, ya ce ya na bukatar gwamnatin tarayya ta ware wani tallafi na musamman, domin taimaka wa mutanen da rikicin ‘yan bindiga ya shafa a jihohin Arewa maso Yammacin Nijeriya uku.

Ya ce idan gwamnatin ta amince, za a yi amfani da kudin ne wajen samar da muhalli da sauran kayayyakin inganta rayuwa ga wadanda rikicin ya shafa, sannan a yi amfani da wani kaso domin biyan jami’an tsaro a jihohin uku.

Masari ya kara da cewa, gwamnatocin jihohin Katsina da Sokoto da Zamfara su na bukatar taimakon kudi domin taimaka wa mutanen da rikicin ya rutsa da su.

Exit mobile version