Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi wa shugaba Muhammadu Buhari hannun ka mai sanda game da abubuwan da ke faruwa a Nijeriya.
A hira da ya yi da kafar yada labarai ta BBC, Bafarawa ya bayyana rashin tsaro a matsayin babbar matsalar da Nijeriya ke fuskanta, inda ya bayyana matsalar garkuwa da mutane a matsayin abin da ya ki ci ya ki cinyewa.
Ya ce bai ga wani ci-gaba da aka samu ba a Nijeriya, ya na mai cewa gara ma gwamnatin baya a kan ta yanzu.
Bafarawa ya kara da cewa, bai taba jin shugaba Buhari ya zauna da gwamnonin Arewa domin tattauna matsaloli da mafitar arewa ba.
You must log in to post a comment.