Ƙungiyar Gamayyar Ma’aikatan Harkokin Man Fetur da Gas NUPENG, ta bayyana goyon bayan cewa za ta shiga cikin zanga-zangar da Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa NLC za ta yi a kan yajin aikin da malaman jami’o’i ke yi a ƙarƙashin ASUU.
Tun farko dai Shugaban kungiyar Kwadago ta kasa Ayuba Wabba, ya ce Ƙungiyar za ta fito zanga-zanga idan yajin aikin ya ƙi ci ya ƙi cinyewa.
An dai shafe tsawon watanni biyar malaman jami’o’i su na yajin aiki, wanda su ka fara tun a ranar 14 Ga Fabrairu.
A cikin wata sanarwa da kungiyar NUPENG ta fitar, ta soki lamirin gwamnatin tarayya, saboda ta kasa magancewa da kuma shawo kan yadda za a daina yajin aikin.
Ta ce za su shiga zanga-zanga domin taya NLC nuna wa gwamnati damuwar su a kan mawuyacin halin da jami’o’in Nijeriya ke ciki.