Home Labarai Kotun Ta Tura Hadimin Tsohon Gwamna Tambuwal Kurkuku

Kotun Ta Tura Hadimin Tsohon Gwamna Tambuwal Kurkuku

217
0
6b9c0c8935573060
6b9c0c8935573060

Kotu ta tura hadimin Tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal, Shafi’u Umar Tureta zuwa gidan gyaran hali bisa zargin ɓatanci ga gwamna mai ci, Ahmad Aliyu, da matarsa, Fatima, a kafafen sada zumunta.

Ana zargin Tureta da yada bayanan karya cewa Gwamna Aliyu ya fadi jarrabawar Turanci a makarantar sakandare da kuma wallafa bidiyon da yake liƙi da daloli a bikin ranar haihuwar Fatima.

An gurfanar da Tureta a kotun majistare a Sakkwato, bayan jami’an tsaro suka kama shi a gidansa.

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International Nigeria, ta yi Allah-wadai da kama Tureta,

sannan ta yi kira a sake shi ba tare da wani sharadi ba, tare da sukar gwamantin Jihar Sakkwato bisa take hakkin dan adam.

Sun bayyana cewa tuhume-tuhumen ba su da tushe, kuma sun bukaci gwamnati ta mayar da hankali kan matsalolin da suka shafi talauci da rashin tsaro a jihar.

Leave a Reply