Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Kotun Duniya Ta Umarci Isra’ila Ta Daina Kai Hari a Gaza Nan Take

thumbs b c 83b182b1b1e352c7e0f81d14014f30e2

thumbs b c 83b182b1b1e352c7e0f81d14014f30e2

kotun Duniya ta umarci Isra’ila ta dakatar da hare-haren da take kai wa a yankin Rafah na Gaza

Afrika ta Kudu ce ta shigar da ƙarar gaban kotun duniya bisa zargin Isra’ila da take yarjejeniyar kisan kiyashi.

Ta ce shiga tsakanin na da muhimmanci domin tseratarwa da kuma kare rayuwar Falasɗinawa.

Kakakin Isra’ila ya ce babu wani mai iko da zai hana ta kare mutanenta da kuma murkushe Hamas a Gaza.

Kotun ICJ ba ta da ikon tursasawa amma duk wani hukunci da ta yi da bai yi wa Isra’ila dadi ba yana da tasiri a idon duniya.

Exit mobile version