Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Kisan Manoman Zabarmari: Boko Haram Ta Dauki Alhakin

Abubakar Shekau, Shugaban Kungiyar Boko Haram

Abubakar Shekau, Shugaban Kungiyar Boko Haram

Kungiyar Boko Haram ta fitar da wani sabon faifen bidiyo da take bayyana cewa ita ke da alhakin kai hari tare da hallaka manoman shinkafa fiye da 40 a kauyen Kosheba da ke Zabarmari a jihar Borno.

Boko Haram ta ce ta hallaka manoman ne saboda sun kama wasu dakarun ta sun mika su a hannun sojin Najeriya da ke gudanar da aiki a yankin.

Da ma dai tun bayan da aka kai harin mutane da dama suka fara zargin cewa mayakan na Boko Haram ne suka aikata mummunar aika-aikar, wanda baya rasa nasaba da yadda ‘yan kungiyar suka dade suna kai irin wadannan hare-hare a yankunan daban-daban na jihar Bornon.

A ranar Asabar din da ta gabata ne maharan suka kai farmaki cikin gonakin a yankin Koshebe na kauyen Zabarmari da ke karamar hukumar mafa a jihar Borno inda suka kashe fiye da mutum 40 ta hanyar yi musu yankan rago.

Exit mobile version