Home Labaru Kewarin Gwiwa: Gwamnatin Kano Zata Ginawa Sojoji Filin Atisaye

Kewarin Gwiwa: Gwamnatin Kano Zata Ginawa Sojoji Filin Atisaye

365
0
Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan Jihar Kano

A ranar Juma’a ne gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya ce gwamnatin jihar zata kashe Naira miliyan 318 wajen gina filin atisaye na sojoji a dajin Falgore inda yanzu yan ta’adda ke fakewa.

Ganduje, ya bayyana hakan ne alokacin rufe bikin gasar sojojin bataliya ta daya da aka gudanar a barikin sojoji ta Bakuvu dake Kano. Yace idan sojoji na a dajin to yan ta’adda da masu gakuwa da mutane da sauran kungiyoyin yan ta’adda zasu ji tsoro su bar wajen.

Gwamnan yace Za a dora tushen ginin wannan muhimmin aiki kwanannan kuma zai zama gagarumar nasara wajen magance matsalolin tsaro a jihar.

Gwamnan ya kara da cewa gasar da sojojin suka gudanar ya kara tabbar da kokarin sojoji na ganin cewa sun magance matsalolin tsaro a kasar nan.

Tun farko, babban sojin bataliyar, Maj-Gen Faruk Yusuf, ya ce gasar na da zummar karawa sojoji sanin dabarun yaki, hadin kai, da kuma shugabanci da dai sauran su.

Leave a Reply