Asusun kula da kananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF, ya ce zai raba wa mata masu juna biyu maganin cuta mai karya garkuwar jiki kyauta a jihar Bauchi.
UNICEF, ta ce za a raba magungunan ne a duk cibiyoyin kiwon lafiya matakin farko guda 323 da ke fadin jihar.
Asusun, ya ce ya yi wannan tanadin ne, ganin cewa cibiyoyin kiwon lafiya matakin farko a jihar su na kula da mata masu juna biyu kyauta.
Shugaban hukumar a Nijeriya reshen jihar Bauchi Bhanu Pathak, ya ce UNICEF ta yi haka ne domin kawo karshen yadda mata ke yawaita haihuwar jarirai dauke da cutar.














































