Home Home INEC Ta Yi Kuskuren Ayyana Abba A Matsayin Gwamnan Kano – Gawuna

INEC Ta Yi Kuskuren Ayyana Abba A Matsayin Gwamnan Kano – Gawuna

13
0
Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar Jam’iyyar APC Dakta Nasir Yusuf Gawuna, ya ce hukumar zabe ta yi kuskure wajen bayyana Abba Kabir na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar sakamakon soke zaben wasu mazabun da aka yi.

Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar Jam’iyyar APC Dakta Nasir Yusuf Gawuna, ya ce hukumar zabe ta yi kuskure wajen bayyana Abba Kabir na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar sakamakon soke zaben wasu mazabun da aka yi.

Yayin ganawa da manema labarai, Gawuna ya ce yawan akwatunan da aka soke ya kai a ce hukumar zabe ta sake gudanar da zabubbuka a wuraren kafin gabatar da kammalallen sakamako da kuma sanar da wanda ya ci.

Gawuna, ya ce duba da yadda hukumar zaben ta bayyana zaben ‘yan majalisun jihar Kano 16 a matsayin wadanda ba su kammala ba, ya dace a ce ta dauki irin wannan matakin a zaben kujerar gwamna.

Ya ce suna da yakinin cewa Allah ke bada mulki ga wanda ya so a lokacin da ya so, don haka za su bi matakan da su ka dace ta fannin shari’a domin neman hakkin su.