Home Labaru Hari: Wani Bam Ya Kashe Mutane A Taron Addini A Afghanistan

Hari: Wani Bam Ya Kashe Mutane A Taron Addini A Afghanistan

191
0

Ma’aikatar tsaron Afganistan ta ce mahara sun dasa bam a
karkashin kujerar wata mota a tsakiyar birnin Ghazni da ke
tsakanin birnin Kabul da Khandahar.

Hukumomin gwamnatin sun tabbatar da mutuwar fararen hula
akalla 15, wasu da dama sun jikkata a sabon harin bam da
mayaka suka tayar yayin da al’ummar musulmi ke taron karatun
Al-Kur’ani.

Sai dai ya zuwa yanzun babu kungiyar da ta dau alhakin harin
amma dama dakarun gwamnati da mayakan Tliban sun sha
dauki ba dadi a lardin Ghazni.

Kuma sabon harin yazo ne bayan wani kazamin harin kunar
bakin wake da ya kashe jami’an tsaro 30.

Duk dai wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da gwamnati ke
shirin sasantawa da mayakan Taliban.