Jam’iyyar adawa a Tanzania ta yi kiran ganggami a yau asabar da nufin nunawa hukumomin kasar cewa ba ta yi na’am da kama jagoran ta ba.
Kusan kwanaki goma kenan da ake tsare da Freeman Mbowe da wasu magoya bayan sa a lokacin da suka yi kokarin gudanar da wani ba bisa ka’aida ba.
Sakatary jam’iyyar ta Chadema mai suna John Mnyika ya musanta tuhumar da ayiwa shugaban jam’iyyar na cewa ya na kokarin rusa zaman lafiya da kasar ke ciki.
Yanzy haka kungiyoyi daga kasashen Duniya na ci gaba da kira ga Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan na ganin ta mutunta dokokin kare bil Adam.