Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Hamayya: Hukumomin Tanzania Na Tsare Da Freeman Mbowe Jagoran Yan Adawa

Jam’iyyar adawa a Tanzania ta yi kiran ganggami a yau asabar da nufin  nunawa hukumomin kasar cewa ba ta yi na’am da kama jagoran ta ba.

Kusan kwanaki goma kenan da ake tsare da  Freeman  Mbowe da wasu magoya bayan sa a lokacin da suka yi kokarin  gudanar da wani  ba bisa ka’aida ba.

Sakatary jam’iyyar ta Chadema mai suna  John Mnyika ya musanta tuhumar da ayiwa shugaban jam’iyyar na cewa ya na kokarin rusa zaman lafiya da kasar ke ciki.

Yanzy haka kungiyoyi daga kasashen Duniya na ci gaba da kira ga Shugabar kasar  Samia Suluhu Hassan na ganin ta mutunta dokokin  kare bil Adam.

Exit mobile version