Home Labaru Gyaran Tarbiyya: Hisbah Ta Kama Mata Masu Zaman Kan Su A Kano

Gyaran Tarbiyya: Hisbah Ta Kama Mata Masu Zaman Kan Su A Kano

361
0
Gwamnatin Jihar Kano
Gwamnatin Jihar Kano

Hukumar Hisbah a jihar Kano ta kama mata da dama masu zaman kan su, a wani mataki na tsabtace jihar kafin Azumin Ramadan na wannan shekarar.

Wata majiya ta ce hukumar ta kai samame ne a gidajen da ake tara mata masu zaman kan su a birnin Kano da wasu kananan hukumomi.

Babban daraktan hukumar ta Hisba a Kano Mallam Abba Sufi, ya ce sun kama Mata masu zaman kan su guda 26 a garin Kano kawai, kuma tuni an gurfanar da wasu daga cikin su a gaban kotu.

Ya ce Kotu ta yanke wa wasu hukuncin daurin shekara daya a karkashin dokar hana karuwanci.

Abba Sufi, ya ce sun kai samame a kananan hukumomin Dawakin Kudu da Tamburawa da su ka yi suna wajen tara mata masu zaman kan su.