Home Labaru Gwamna Raɗɗa Ya Yi Naɗe-Naɗen Farko

Gwamna Raɗɗa Ya Yi Naɗe-Naɗen Farko

1
0

Sabon gwamnan Jihar Katsina Dakta Dikko Umar Raɗɗa, ya
yi sabbin naɗe-naɗen da su ka haɗa da Sakataren Gwamnati
da Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Jihar da Daraktan
Yaɗa Labarai da sauran su.

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Gwamna Raɗɗa ya naɗa Ahmed Musa Ɗangiwa a matsayin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, yayin da Alhaji Jabiru Tsauri ya zama Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnati, sai kuma Barista Muhtar Aliyu Saulawa da aka nada a matsayin mataimakin shugaban ma’aikatan fadar gwamnati, da Alhaji Abdullahi Aliyu Turaji a matsayin Babban Sakataren Ofishin Gwamna.

Sauran sun hada da Malam Maiwada Ɗan Malam a matsayin Babban Daraktan Yaɗa Labarai, da Ibrahim Kaula Mohammed a matsayin Babban Sakataren Yaɗa Labarai.

Gwamna Dikko Radda, ya kuma naɗa Alhaji Bishir Maikano a matsayin Babban Mataimaki na Musamman a kan Tsare- tsaren fadar gwamnati.

Dikko Raɗɗa, ya taya waɗanda naɗin ya shafa murna, sannan ya bukaci su hada kai da shi domin ganin an dawo da martabar jihar Katsina.