Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Gargadi: Kada A Maida Mutuwar Funke Olakunri Siyasa – Buhari

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya gargaɗi ‘yan Nijeriya su riƙa tauna magana kafin su furta ta, musamman a wannan lokaci da ake fama da matsalar tsaro.

Buhari ya bayyana haka ne, a cikin wata sanarwa da mai taimaka ma shi ta fuskar yada labarai da hulda da jama’a Garba Shehu ya fitar.

Garba Shehu And president Buhari

Shugaba Buhari, ya ce bai dace a ce waɗanda su ke kan madafun iko kuma shugabannin al’umma su na furta maganganu ba tare da tauna su ba.

Ya ce dole ne shugabanni su zo a haɗa kai wajen ganin an shawo kan matsalar tsaro da ake fama da ita a Nijeriya ba a riƙa magana da son rai ba.

Da ya ke tsokaci a kan yadda ake alakanta matsalar tsaro da siyasa a Nijeriya, shugaba Buhari ya ce yin hakan ba abu ne da ya dace a ce ana yi ba.

Exit mobile version