Site icon Liberty TV/Radio Hausa – Labaru – Tashar 'Yanci!

Ganduje Ya Ce ‘Yan Bindiga Sun Kwace Dajin Falgore

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya koka kan yadda ‘yan bindiga suka mamaye dajin Falgore.

Gwamnan wanda ya zanta da manema labarai a fadar shugaban kasa bayan ganawar sa da shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Juma’a, ya bukaci gwamnatin tarayya ta kawo agaji ga jihar Kano da wasu jihohi uku da suka raba dajin.

Gnaduje, ya bayyana kalubalen tsaro da ake fuskanta a kasar a matsayin abin takaici.

Exit mobile version